as-Saffat (الصَّافَّات)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 37 • 182 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
37:1 Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
37:2 Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
37:3 Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
37:4 Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
37:5 Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
37:6 Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
37:7 Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
37:8 Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
37:9 Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
37:10 Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
37:11 Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
37:12 Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
37:13 Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
37:14 Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
37:15 Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
37:16 "Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
37:17 "Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
37:18 Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
37:19 Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
37:20 Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
37:21 Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
37:22 Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
37:23 Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
37:24 Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
37:25 Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
37:26 Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
37:27 Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
37:28 Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
37:29 Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
37:30 "Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
37:31 "Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
37:32 "Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
37:33 To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
37:34 Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
37:35 Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
37:36 Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
37:37 Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
37:38 Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
37:39 Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
37:40 Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:41 Waɗannan sunã da abinci sananne.
37:42 'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
37:43 A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
37:44 A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
37:45 Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
37:46 Farã mai dãɗi ga mashãyan.
37:47 A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
37:48 Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
37:49 Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
37:50 Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
37:51 Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
37:52 Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
37:53 "Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
37:54 (Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
37:55 Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
37:56 Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
37:57 "Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
37:58 "Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
37:59 "Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
37:60 Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
37:61 Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
37:62 Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
37:63 Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
37:64 Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
37:65 Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
37:66 To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
37:67 Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
37:68 Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
37:69 Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
37:70 Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
37:71 Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
37:72 Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
37:73 Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
37:74 Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:75 Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
37:76 Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
37:77 Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
37:78 Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
37:79 Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
37:80 Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:81 Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:82 Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
37:83 Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
37:84 A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
37:85 A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
37:86 "Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
37:87 "To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
37:88 Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
37:89 Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
37:90 Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
37:91 Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
37:92 "Me ya sãme ku, bã ku magana?"
37:93 Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
37:94 Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
37:95 Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
37:96 "Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
37:97 Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
37:98 Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
37:99 Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
37:100 "Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
37:101 Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
37:102 To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
37:103 To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
37:104 Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
37:105 "Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:106 Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
37:107 Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
37:108 Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
37:109 Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
37:110 Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:111 Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:112 Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
37:113 Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
37:114 Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
37:115 Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
37:116 Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
37:117 Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
37:118 Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
37:119 Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
37:120 Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
37:121 Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:122 Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
37:123 Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:124 A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
37:125 "Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
37:126 "Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
37:127 Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
37:128 Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:129 Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
37:130 Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
37:131 Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
37:132 Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
37:133 Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:134 A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
37:135 Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
37:136 Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
37:137 Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
37:138 Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
37:139 Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
37:140 A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
37:141 Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
37:142 Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
37:143 To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
37:144 Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
37:145 Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
37:146 Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
37:147 Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
37:148 Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
37:149 Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
37:150 Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
37:151 To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
37:152 "Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
37:153 Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
37:154 Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
37:155 Shin, bã ku tunãni?
37:156 Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
37:157 To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
37:158 Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
37:159 Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
37:160 Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
37:161 To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
37:162 Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
37:163 Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
37:164 "Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
37:165 "Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
37:166 "Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
37:167 Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
37:168 "Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
37:169 "Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
37:170 Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
37:171 Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
37:172 Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
37:173 Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
37:174 Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
37:175 Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
37:176 Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
37:177 To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
37:178 Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
37:179 Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
37:180 Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
37:181 Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
37:182 Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.