al-Waqi`ah (الوَاقِعَة)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 56 • 96 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
56:1 Idan mai aukuwa ta auku.
56:2 Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
56:3 (Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
56:4 Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
56:5 Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
56:6 Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
56:7 Kuma kun kasance nau'i uku.
56:8 Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
56:9 Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
56:10 Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
56:11 Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
56:12 A ckin Aljannar ni'ima.
56:13 Jama'a ne daga mutãnen farko.
56:14 Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
56:15 (Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
56:16 Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
56:17 Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
56:18 Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
56:19 Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
56:20 Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
56:21 Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
56:22 Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
56:23 Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
56:24 A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
56:25 Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
56:26 Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
56:27 Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
56:28 (Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
56:29 Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
56:30 Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
56:31 Da wani ruwa mai gudãna.
56:32 Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
56:33 Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.
56:34 Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
56:35 Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
56:36 Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
56:37 Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
56:38 Ga mazõwa dãma.
56:39 Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.
56:40 Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
56:41 Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?
56:42 Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
56:43 Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.
56:44 Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.
56:45 Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
56:46 Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.
56:47 Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
56:48 "Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
56:49 Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."
56:50 "Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."
56:51 "Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
56:52 "Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
56:53 "Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
56:54 "Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
56:55 "Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
56:56 Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
56:57 Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
56:58 Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
56:59 Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
56:60 Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,
56:61 A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
56:62 Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
56:63 Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
56:64 Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
56:65 Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
56:66 (Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
56:67 "Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
56:68 Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
56:69 Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
56:70 Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
56:71 Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
56:72 Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
56:73 Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
56:74 Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
56:75 To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
56:76 Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
56:77 Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
56:78 A cikin wani littafi tsararre.
56:79 Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.
56:80 Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.
56:81 Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
56:82 Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
56:83 To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
56:84 Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
56:85 Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.
56:86 To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
56:87 Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
56:88 To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,
56:89 Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
56:90 Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,
56:91 Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
56:92 Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,
56:93 Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.
56:94 Da ƙõnuwa da Jahĩm,
56:95 Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.
56:96 Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.