al-Hijr (الحِجْر)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 15 • 99 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
15:1 A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
15:2 Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
15:3 Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
15:4 Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
15:5 Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
15:6 Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
15:7 "Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
15:8 Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
15:9 Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
15:10 Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
15:11 Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
15:12 Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
15:13 Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
15:14 Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
15:15 Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
15:16 Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
15:17 Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
15:18 Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
15:19 Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
15:20 Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
15:21 Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
15:22 Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
15:23 Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
15:24 Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
15:25 Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
15:26 Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
15:27 Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
15:28 Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
15:29 "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
15:30 Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
15:31 Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
15:32 Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
15:33 Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
15:34 Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
15:35 "Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
15:36 Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
15:37 Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
15:38 "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
15:39 Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
15:40 "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
15:41 Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
15:42 "Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
15:43 Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
15:44 Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
15:45 Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
15:46 "Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
15:47 Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
15:48 Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
15:49 Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
15:50 Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
15:51 Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
15:52 A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
15:53 Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
15:54 Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
15:55 Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
15:56 Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
15:57 Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
15:58 Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
15:59 "Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
15:60 "Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
15:61 To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
15:62 Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
15:63 Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
15:64 "Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
15:65 "Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
15:66 Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
15:67 Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
15:68 Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
15:69 "Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
15:70 Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
15:71 Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
15:72 Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
15:73 Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
15:74 Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
15:75 Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
15:76 Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
15:77 Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
15:78 Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
15:79 Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
15:80 Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
15:81 Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
15:82 Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
15:83 Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
15:84 Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
15:85 Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
15:86 Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
15:87 Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
15:88 Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
15:89 Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
15:90 Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
15:91 Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
15:92 To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
15:93 Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
15:94 Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
15:95 Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
15:96 Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
15:97 Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
15:98 Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
15:99 Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.