15:1
                                        
                                    
                                    A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:2
                                        
                                    
                                    Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:3
                                        
                                    
                                    Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:4
                                        
                                    
                                    Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:5
                                        
                                    
                                    Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:6
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:7
                                        
                                    
                                    "Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:8
                                        
                                    
                                    Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:9
                                        
                                    
                                    Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:10
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:11
                                        
                                    
                                    Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:12
                                        
                                    
                                    Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:13
                                        
                                    
                                    Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:14
                                        
                                    
                                    Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:15
                                        
                                    
                                    Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:16
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:17
                                        
                                    
                                    Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:18
                                        
                                    
                                    Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:19
                                        
                                    
                                    Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:20
                                        
                                    
                                    Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:21
                                        
                                    
                                    Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:22
                                        
                                    
                                    Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:23
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:24
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:25
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:26
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:27
                                        
                                    
                                    Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:28
                                        
                                    
                                    Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:29
                                        
                                    
                                    "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:30
                                        
                                    
                                    Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:31
                                        
                                    
                                    Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:32
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:33
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:34
                                        
                                    
                                    Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:35
                                        
                                    
                                    "Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:36
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:37
                                        
                                    
                                    Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:38
                                        
                                    
                                    "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:39
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:40
                                        
                                    
                                    "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:41
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:42
                                        
                                    
                                    "Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:43
                                        
                                    
                                    Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:44
                                        
                                    
                                    Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:45
                                        
                                    
                                    Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:46
                                        
                                    
                                    "Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:47
                                        
                                    
                                    Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:48
                                        
                                    
                                    Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:49
                                        
                                    
                                    Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:50
                                        
                                    
                                    Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:51
                                        
                                    
                                    Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:52
                                        
                                    
                                    A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:53
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:54
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:55
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:56
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:57
                                        
                                    
                                    Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:58
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:59
                                        
                                    
                                    "Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:60
                                        
                                    
                                    "Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:61
                                        
                                    
                                    To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:62
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:63
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:64
                                        
                                    
                                    "Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:65
                                        
                                    
                                    "Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:66
                                        
                                    
                                    Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:67
                                        
                                    
                                    Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:68
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:69
                                        
                                    
                                    "Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:70
                                        
                                    
                                    Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:71
                                        
                                    
                                    Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:72
                                        
                                    
                                    Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:73
                                        
                                    
                                    Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:74
                                        
                                    
                                    Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:75
                                        
                                    
                                    Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:76
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:77
                                        
                                    
                                    Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:78
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:79
                                        
                                    
                                    Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:80
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:81
                                        
                                    
                                    Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:82
                                        
                                    
                                    Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:83
                                        
                                    
                                    Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:84
                                        
                                    
                                    Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:85
                                        
                                    
                                    Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:86
                                        
                                    
                                    Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:87
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:88
                                        
                                    
                                    Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:89
                                        
                                    
                                    Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:90
                                        
                                    
                                    Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:91
                                        
                                    
                                    Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:92
                                        
                                    
                                    To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:93
                                        
                                    
                                    Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:94
                                        
                                    
                                    Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:95
                                        
                                    
                                    Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:96
                                        
                                    
                                    Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:97
                                        
                                    
                                    Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:98
                                        
                                    
                                    Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
                                
                                
                        
                                    
                                        
                                            15:99
                                        
                                    
                                    Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.