15:1
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
15:2
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
15:3
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
15:4
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
15:5
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
15:6
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
15:7
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
15:8
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
15:9
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
15:10
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
15:11
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
15:12
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
15:13
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
15:14
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
15:15
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
15:16
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
15:17
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
15:18
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
15:19
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
15:20
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
15:21
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
15:22
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
15:23
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
15:24
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
15:25
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
15:26
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
15:27
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
15:28
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
15:29
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
15:30
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
15:31
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
15:32
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
15:33
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
15:34
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
15:35
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
15:36
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
15:37
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
15:38
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
15:39
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
15:40
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
15:41
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
15:42
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
15:43
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
15:44
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
15:45
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
15:46
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
15:47
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
15:48
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
15:49
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
15:50
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
15:51
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
15:52
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
15:53
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
15:54
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
15:55
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
15:56
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
15:57
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
15:58
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
15:59
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
15:60
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
15:61
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
15:62
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
15:63
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
15:64
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
15:65
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
15:66
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
15:67
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
15:68
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
15:69
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
15:70
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
15:71
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
15:72
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
15:73
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
15:74
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
15:75
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
15:76
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
15:77
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
15:78
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
15:79
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
15:80
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
15:81
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
15:82
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
15:83
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
15:84
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
15:85
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
15:86
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
15:87
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
15:88
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
15:89
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
15:90
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
15:91
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
15:92
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
15:93
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
15:94
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
15:95
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
15:96
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
15:97
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
15:98
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
15:99
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.