al-Haqqah (الحَاقَّة)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 69 • 52 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
69:1 Kiran gaskiya!
69:2 Mẽne ne kiran gaskiya?
69:3 Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
69:4 Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
69:5 To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
69:6 Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
69:7 (Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
69:8 To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
69:9 Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
69:10 Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
69:11 Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
69:12 Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
69:13 To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
69:14 Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
69:15 A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
69:16 Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
69:17 Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
69:18 A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
69:19 To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
69:20 "Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
69:21 Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
69:22 A cikin Aljanna maɗaukakiya.
69:23 Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
69:24 (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
69:25 Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
69:26 "Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
69:27 "In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
69:28 "Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
69:29 "Ĩkona ya ɓace mini!"
69:30 (Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
69:31 "Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
69:32 "Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
69:33 "Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
69:34 "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
69:35 "Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
69:36 "Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
69:37 "Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
69:38 To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
69:39 Da abin da bã ku iya gani.
69:40 Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
69:41 Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
69:42 Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
69:43 Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
69:44 Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
69:45 Dã Mun kãma shi da dãma.
69:46 sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
69:47 Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
69:48 Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
69:49 Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
69:50 Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
69:51 Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
69:52 Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.