al-Qalam (القَلَم)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 68 • 52 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
68:1 Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
68:2 Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
68:3 Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
68:4 Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
68:5 Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
68:6 Ga wanenku haukã take.
68:7 Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
68:8 Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
68:9 Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
68:10 Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
68:11 Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
68:12 Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
68:13 Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
68:14 Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
68:15 Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
68:16 Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
68:17 Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
68:18 Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
68:19 Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
68:20 Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
68:21 Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
68:22 Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
68:23 Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
68:24 "Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
68:25 Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
68:26 Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
68:27 "Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
68:28 Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
68:29 Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
68:30 Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
68:31 Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
68:32 "Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
68:33 Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
68:34 Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
68:35 Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
68:36 Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
68:37 Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
68:38 Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
68:39 Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
68:40 Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
68:41 Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
68:42 Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
68:43 Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
68:44 Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
68:45 Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
68:46 Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
68:47 Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
68:48 Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
68:49 Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
68:50 Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
68:51 Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
68:52 Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.