70:1
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
70:2
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
70:3
Daga Allah Mai matãkala.
70:4
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
70:5
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
70:6
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
70:7
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
70:8
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
70:9
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
70:10
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
70:11
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
70:12
Da matarsa da ɗan'uwansa.
70:13
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
70:14
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
70:15
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
70:16
Mai twãle fãtar goshi.
70:17
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
70:18
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
70:19
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
70:20
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
70:21
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
70:22
Sai mãsu yin salla,
70:23
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
70:24
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
70:25
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
70:26
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
70:27
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
70:28
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
70:29
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
70:30
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
70:31
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
70:32
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
70:33
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
70:34
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
70:35
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
70:36
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
70:37
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
70:38
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
70:39
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
70:40
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
70:41
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
70:42
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
70:43
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
70:44
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)