al-Ma`arij (المَعَارِج)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 70 • 44 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
70:1 Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
70:2 Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
70:3 Daga Allah Mai matãkala.
70:4 Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
70:5 Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
70:6 Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
70:7 Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
70:8 Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
70:9 Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
70:10 Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
70:11 Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
70:12 Da matarsa da ɗan'uwansa.
70:13 Da danginsa, mãsu tattarã shi.
70:14 Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
70:15 A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
70:16 Mai twãle fãtar goshi.
70:17 Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
70:18 Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
70:19 Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
70:20 Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
70:21 Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
70:22 Sai mãsu yin salla,
70:23 Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
70:24 Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
70:25 Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
70:26 Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
70:27 Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
70:28 Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
70:29 Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
70:30 Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
70:31 To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
70:32 Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
70:33 Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
70:34 Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
70:35 Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
70:36 Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
70:37 Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
70:38 Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
70:39 A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
70:40 Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
70:41 Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
70:42 Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
70:43 Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
70:44 Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)