80:1
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
80:2
Sabõda makãho yã je masa.
80:3
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
80:4
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
80:5
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
80:6
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
80:7
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
80:8
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
80:9
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
80:10
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
80:11
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
80:12
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
80:13
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
80:14
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
80:15
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
80:16
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
80:17
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
80:18
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
80:19
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
80:20
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
80:21
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
80:22
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
80:23
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
80:24
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
80:25
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
80:26
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
80:27
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
80:28
Da inabi da ciyãwa.
80:29
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
80:30
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
80:31
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
80:32
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
80:33
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
80:34
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
80:35
Da uwarsa da ubansa.
80:36
Da mãtarsa da ɗiyansa.
80:37
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
80:38
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
80:39
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
80:40
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
80:41
Baƙi zai rufe su.
80:42
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).