at-Takwir (التَّكْوِير)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 81 • 29 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
81:1 Idan rãna aka shafe haskenta
81:2 Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
81:3 Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
81:4 Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
81:5 Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
81:6 Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
81:7 Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
81:8 Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
81:9 "Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
81:10 Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
81:11 Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
81:12 Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
81:13 Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
81:14 Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
81:15 To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
81:16 Mãsu gudu suna ɓũya.
81:17 Da dare idan ya bãyar da bãya.
81:18 Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
81:19 Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
81:20 Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
81:21 Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
81:22 Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
81:23 Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
81:24 Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
81:25 Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
81:26 Shin, a inã zã ku tafi?
81:27 Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
81:28 Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
81:29 Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.