81:1
Idan rãna aka shafe haskenta
81:2
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
81:3
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
81:4
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
81:5
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
81:6
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
81:7
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
81:8
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
81:9
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
81:10
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
81:11
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
81:12
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
81:13
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
81:14
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
81:15
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
81:16
Mãsu gudu suna ɓũya.
81:17
Da dare idan ya bãyar da bãya.
81:18
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
81:19
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
81:20
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
81:21
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
81:22
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
81:23
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
81:24
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
81:25
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
81:26
Shin, a inã zã ku tafi?
81:27
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
81:28
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
81:29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.