al-Infitar (الإِنْفِطَار)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 82 • 19 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
82:1 Idan sama ta tsãge.
82:2 Kuma idan taurãri suka wãtse.
82:3 Kuma idan tẽkuna aka facce su.
82:4 Kuma idan kaburbura aka tõne su.
82:5 Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
82:6 Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
82:7 Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
82:8 A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
82:9 A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
82:10 Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
82:11 Mãsu daraja, marubũta.
82:12 Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
82:13 Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
82:14 Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
82:15 Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
82:16 Bã zã su faku daga gare ta ba.
82:17 Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?
82:18 Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
82:19 Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.