al-Ghashiyah (الغَاشِيَة)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 88 • 26 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
88:1 Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?
88:2 Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.
88:3 Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.
88:4 Zã su shiga wata wuta mai zãfi.
88:5 Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.
88:6 Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.
88:7 Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.
88:8 Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.
88:9 Game da aikinsu, masu yarda ne.
88:10 (Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.
88:11 Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.
88:12 A cikinta akwai marmaro mai gudãna.
88:13 A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.
88:14 Da kõfuna ar'aje.
88:15 Da filõli jẽre,
88:16 Da katifu shimfiɗe.
88:17 Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?
88:18 Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?
88:19 Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?
88:20 Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?
88:21 sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.
88:22 Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.
88:23 Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.
88:24 To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.
88:25 Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.
88:26 Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.