84:1
Idan sama ta kẽce,
84:2
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
84:3
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
84:4
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
84:5
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
84:6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
84:7
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
84:8
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
84:9
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
84:10
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
84:11
To, zã shi dinga kiran halaka!
84:12
Kuma ya shiga sa'ĩr.
84:13
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
84:14
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
84:15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
84:16
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
84:17
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
84:18
Da watã idan (haskensa) ya cika.
84:19
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
84:20
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
84:21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
84:22
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
84:23
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
84:24
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
84:25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.