96:1
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
96:2
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
96:3
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
96:4
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
96:5
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
96:6
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
96:7
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
96:8
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
96:9
Shin, kã ga wanda ke hana.
96:10
Bãwã idan yã yi salla?
96:11
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
96:12
Ko ya yi umurni da taƙawa?
96:13
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
96:14
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
96:15
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
96:16
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
96:17
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
96:18
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
96:19
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).