al-`Adiyat (العَادِيَات)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 100 • 11 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
100:1 Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.
100:2 Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.
100:3 Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.
100:4 Sai su motsar da ƙũra game da shi.
100:5 Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.
100:6 Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.
100:7 Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.
100:8 Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.
100:9 Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.
100:10 Aka bayyana abin da ke cikin zukata.
100:11 Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?