az-Zalzalah (الزَّلْزَلَة)

Abubakar Mahmoud Gumi - Abubakar Mahmoud Gumi

Chapter 99 • 8 verses • Meccan

← Previous Chapter Next Chapter →
99:1 Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
99:2 Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
99:3 Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
99:4 A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
99:5 cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
99:6 A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
99:7 To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
99:8 Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.