Chapter 1 • 7 verses • Meccan
Next Chapter →
1:1
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1:2
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;
1:3
Mai rahama, Mai jin ƙai;
1:4
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.
1:5
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.
1:6
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.
1:7
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.